Rikicin PDP Ya Ƙara Ɓullo Wa Yayin Da Wike Ya Nemi A Tabbatar Da Zaben Yankin Kudu-Maso-Gabashin Jam’iyyar

uploads/images/newsimages/KatsinaTimes20082025_124338_FB_IMG_1755693764844.jpg


Daga Wakilinmu | Katsina Times 

Rikicin cikin gida na jam’iyyar adawa ta Peoples Democratic Party (PDP) ya sake kunno kai, bayan sabon matsayi daga Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, wanda ya nace cewa dole ne jam’iyyar ta amince da sakamakon babban taron yankin Kudu-Maso-Gabashin da aka gudanar a Calabar.

A cikin hira da manema labarai da ya saba yi a Abuja a farkon wannan wata, Wike ya bayyana cewa rikicin PDP ya lafa “a yanzu,” amma ya jaddada cewa dole ne a tabbatar da nasarar zaben da ya sake zabar Chief Dan Orbih a matsayin Mataimakin Shugaban Jam’iyyar na ƙasa (Kudu-Maso-Gabashi).

“Zaben mu na yankin Kudu-Maso-Gabashi da aka gudanar dole ne a tabbatar da shi. Ba wata hanya biyu a kai ba,” in ji Wike, yana gargadin cewa rashin amincewa da sakamakon na iya tayar da sabuwar fitina.

Wike ya yi Allah wadai da yunkurin soke sakamakon taron bayan wata wasika ta isa hukumar INEC da ta yi ikirarin cewa an dage taron. Ya ce babu amfani a soke taron da kotu ta riga ta ba da izini.

Duk da kasancewarsa a majalisar ministocin Shugaba Bola Tinubu, Wike ya karyata jita-jitar cewa zai fice daga PDP zuwa jam’iyyar APC.
“Ba zan bar wannan jam’iyya, PDP, wadda na sadaukar da komai a cikinta, in koma ga barayi da masu tsotsa jini ba,” in ji shi.

Sai dai wasu manyan jami’an PDP sun yi watsi da matsayar Wike. Mamba a kwamitin zartarwa na kasa (NEC), Timothy Osadolor, ya bayyana cewa kwamitin rikon kwarya na yankin Kudu-Maso-Gabashi yana nan daram kuma bisa tsarin doka.

“Dokar jam’iyya ta fayyace yadda ake gudanar da zabukan yankuna. Duk wanda yake son tsayawa takara dole ne ya bi ka’idoji. Abin da ya dace shi ne neman goyon baya, ba sanya sharudda ga jam’iyya ba,” in ji shi.

Shi ma shugaban kwamitin rikon kwarya na yankin, Emmanuel Ogidi, ya ce Wike kawai yana “barazana” ne.
“Kwamitin Aiki na Ƙasa (NWC) shi ne ya amince ya kuma rantsar da mu saboda ba a gudanar da abin da ya dace a yankin Kudu-Maso-Gabashi ba. Wa'adin mu na watanni uku bai ƙare ba. Jam’iyya ta kafa mu bisa kundin tsarin mulki, ba maganar minista ba,” in ji Ogidi.

Rahotanni sun nuna cewa damuwa na ƙaruwa a PDP yayin da wa’adin kwamitin gudanarwa na ƙasa ke gab da ƙarewa a watan Disamba. An riga an amince da jadawalin babban taron zabukan jam’iyyar da za a gudanar a watan Nuwamba a Ibadan.

Ko da yake an samu ɗan sasanci bayan amincewa da Sanata Samuel Anyanwu, abokin siyasar Wike, a matsayin Sakataren Ƙasa na jam’iyyar, akwai fargabar cewa sabon sabani kan shugabancin yankin Kudu-Maso-Gabashi zai sake haddasa rikici.

Jiga-jigan jam’iyyar sun sha alwashin cewa ba za su bar Wike ya ƙayyade shugabanci a yankin ba, abin da ke iya zama sabon fada kafin babban taron jam’iyyar a Nuwamba.

Follow Us